Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya yaba da kafa Kwalejin Barefoot Renewable Energy da ke Osara a Jihar Kogi, yana mai bayyana ta a matsayin wani muhimmin mataki na bunƙasa ƙwararrun ma'aikata a fannin makamashi mai sabuntawa.

Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Ahmed Tinubu a wajen ƙaddamar da kwalejin, ya ce cibiyar za ta taka muhimmiyar rawa wajen horar da matasa da ƙwararru da za su jagoranci ci gaban fasahar makamashi mai sabuntawa a Najeriya.

Ya bayyana cewa kwalejin za ta samar da ƙwararrun masu aikin fasaha, masu sarrafa na'urori da kuma masu kula da gyaran kayayyakin makamashi, domin su samu ilimi da ƙwarewar da za ta ba su damar yin gogayya a matakin duniya.

Mataimakin Shugaban Ƙasar ya ƙara da cewa kafa wannan kwaleji na nuna aniyar gwamnatin tarayya na zuba jari a ilimi, ƙwarewar sana'o'i da makamashi mai tsafta domin bunƙasa tattalin arziki da samar da ayyukan yi ga matasan Najeriya.