Rahotanni sun nuna cewa gwamnatin Shugaban Amurka, Donald Trump, na shirin tura wasu ‘yan ciranin Iran tare da wasu baki daga ƙasashe daban-daban zuwa Central African Republic a ƙarƙashin wata sabuwar yarjejeniya ta korar baki zuwa ƙasa ta uku.

A cewar rahotanni, mutanen da ake shirin korawa sun haɗa da ‘yan Iran, Syria, Afghanistan da kuma wani ɗan ƙasar Turkiyya. Wasu daga cikin ‘yan Iran ɗin sun nemi mafaka a Amurka, kuma lauyoyinsu sun ce suna fargabar fuskantar tsangwama ko azabtarwa idan aka mayar da su ƙasarsu.

Rahotannin sun ce jirgin farko na iya ɗaukar kusan mutum 20 zuwa babban birnin ƙasar, Bangui, yayin da ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam ke nuna damuwa kan tura mutane zuwa ƙasar da ke fama da talauci da matsalolin tsaro.

Matakin na daga cikin manufofin gwamnatin Trump na amfani da yarjejeniyoyin “ƙasa ta uku” wajen korar baƙin da ba za a iya mayar da su kai tsaye zuwa ƙasashensu ba.