Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya yi gargaɗi ga duk wanda ke taimaka wa ’yan bindiga ta hanyar ba su bayanai, yana mai cewa gwamnati ba za ta yi ƙasa a gwiwa ba wajen hukunta duk wanda aka samu da hannu a irin waɗannan ayyuka.

‎Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wani taron gaggawa na tsaro da aka gudanar a Fadar Gwamnati da ke Birnin Kebbi, bayan sake barkewar hare-haren ’yan bindiga a wasu sassan jihar.

‎Ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da yin aiki kafada da kafada da jami’an tsaro domin dakile ayyukan masu tayar da ƙayar baya.

‎Nasir Idris ya jaddada cewa ba za a yi afuwa ga duk wanda aka kama yana ba ’yan bindiga bayanai ko wata gudummawa ba, yana mai cewa duk wanda aka samu da laifi zai fuskanci hukunci bisa tanadin doka.