Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Katsina United FC ta sanar da rasuwar ɗan wasanta, Ozoh Chinedu, wanda ya rasu a lokacin wani wasan sada zumunta na share fage a ranar Talata.
Ozoh yana cikin ‘yan wasan Katsina United da suka buga wasan sada zumunta da Niger Tornadoes FC a ranar Talata, a filin wasa na Muhammadu Dikko da ke Katsina.
Ozoh ya koma Katsina United FC ne bayan ya bar wata ƙungiyar ƙwallon ƙafa da ke Arewacin Najeriya, wato Kano Pillars FC.
Hukumar yaɗa labarai ta ƙungiyar Katsina United ce ta bayyana rasuwar ɗan wasan a cikin wata sanarwa mai taken “Labari mai ɗaga hankali: Ɗan wasan Katsina United Ozoh Chinedu ya rasu a lokacin wasan sada zumunta na share fage”, wadda ta wallafa a shafinta na Facebook a ranar Talata.
A lokacin wasan ne Ozoh ya samu matsalar lafiya, lamarin da ya sa aka garzaya da shi wani asibitin ƙwararru domin samun kulawar gaggawa.
Sanarwar ta ce al’ummar ƙwallon ƙafa a Jihar Katsina da ma sauran sassan ƙasar sun shiga cikin jimami sakamakon rasuwar kwatsam ta Ozoh, sabon ɗan wasan Katsina United kuma tsohon ɗan wasan Kano Pillars FC.
“Rahotanni sun bayyana cewa Ozoh ya rasu a farkon sa’o’in ranar Talata, 11 ga Agusta, 2026, bayan an garzaya da shi K-Dara Specialist Hospital da ke Katsina, sakamakon wata matsalar lafiya da ta same shi a lokacin wasan sada zumunta tsakanin Katsina United da Niger Tornadoes FC a filin wasa na Muhammadu Dikko, Katsina,” in ji sanarwar.