Mataimakin Shugaban Najeriya, Kashim Shettima, zai shafe makonni biyu yana karatu da yin nazari kan rayuwa da harkokin shugabanci yayin hutunsa na makonni biyu.

Mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha, ya bayyana cewa hutun zai ba Shettima damar zurfafa ilimi da kuma yin tunani kan muhimman batutuwan da suka shafi aikinsa da hidimarsa ga Najeriya.

Ya ce Shettima ya saba amfani da irin wannan lokaci wajen karatu, nazari da koyon sabbin abubuwa, yana mai cewa shugabanci mai ɗorewa na buƙatar mutum ya ci gaba da neman ilimi a kowane lokaci.

Nkwocha ya ƙara da cewa nisantar ayyukan yau da kullum na ɗan lokaci na ba wa shugaba damar sake duba ra’ayoyi da tsare-tsare cikin natsuwa, domin komawa bakin aiki da sabbin tunani da dabaru.

Ya ce samun babban matsayi ba yana nufin mutum ya daina koyo ba, sai dai ƙarin nauyin da ke tattare da shugabanci yana ƙara nuna muhimmancin ci gaba da neman ilimi.

A cewarsa, wannan lokaci na karatu da nazari zai taimaka wa Shettima wajen ƙara fahimta da ƙwarewar da ake buƙata domin ci gaba da yi wa Najeriya hidima.