Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya umarci Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Ƙasa Ta'annati (EFCC) da ta gaggauta komawa kotu domin neman a soke umarnin da ya ba ta damar rufe asusun gwamnatin Jihar Osun.
A cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Alhamis, shugaban ya bayyana rashin jin daɗinsa kan lokacin da aka ɗauki matakin, yana mai cewa hakan ya ba shi kunya.
"Dole ne in bayyana cewa abin ya ba ni kunya ƙwarai. Ba wai saboda EFCC ta aiwatar da aikinta ba ne bisa umarnin kotu, sai dai saboda lokacin da ta ɗauki wannan mataki," in ji Tinubu.
Shugaban ya ce duk wani mataki da hukumomin gwamnatin tarayya suka ɗauka, jama'a kan danganta shi da shugaban ƙasa, ko da kuwa bai da masaniya kan aiwatar da shi.
Ya kuma jaddada cewa tun bayan hawansa mulki, ya kauce wa tsoma baki cikin ayyukan EFCC da sauran hukumomin bincike domin su gudanar da aikinsu cikin 'yanci da ƙwarewa.
A cewarsa, hukumomin yaƙi da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tabbatar da doka ya kamata su ci gaba da gudanar da ayyukansu ba tare da tsoro, son rai ko katsalandan na siyasa ba.
Sai dai Tinubu ya ce, duk da cewa bai samu cikakken bayani kan dalilan da suka sa EFCC ta nemi umarnin kotu na rufe asusun gwamnatin Jihar Osun ba, yana ganin lokacin da aka ɗauki matakin bai dace ba.
Ya bayyana cewa kasancewar Jihar Osun na dab da gudanar da zaɓen gwamna, ya kamata a guji duk wani mataki da zai iya haifar da zargin cewa ana amfani da hukumomin gwamnatin tarayya wajen yin katsalandan a harkokin zaɓe.
Saboda haka, shugaban ya ce ya umarci EFCC da ta gaggauta komawa kotu domin neman a soke umarnin rufe asusun, tare da dakatar da duk wani mataki da aka ɗauka kan gwamnatin jihar dangane da wannan lamari.
EFCC ta samu umarnin kotu na rufe asusun gwamnatin Jihar Osun a ranar 5 ga Agustan 2026. Sai dai zuwa lokacin wallafa wannan rahoto, hukumar ba ta fitar da cikakken bayani kan dalilan da suka sa ta nemi wannan umarni ba.