Wani bincike da kafar yaɗa labarai ta Lighthouse Reports tare da jaridar Financial Times suka wallafa a ranar 30 ga Yuli, ya yi zargin cewa an fitar da tsakanin tan dubu biyu zuwa dubu biyar na ma'adinin uranium daga Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo zuwa China ta hanyar da ba a bayyana ba.
Rahoton ya ce an ɓoye uranium ɗin ne cikin jigilar ma'adinin cobalt, wanda Congo ke fitarwa zuwa ƙasashen waje. Binciken ya yi nuni da cewa alkaluman Hukumar Kula da Makamashin Nukiliya ta Duniya (IAEA) na shekarar 2024 sun nuna yiwuwar irin wannan safara.
A cewar rahoton, an samo uranium ɗin ne daga wata mahaƙar ma'adinin cobalt da ke lardin Katanga, inda ake zargin an haɗa shi da cobalt kafin a fitar da shi zuwa China ba tare da an bayyana hakan ba.
Binciken ya kuma nuna cewa daga shekarar 2009 zuwa 2023, yawan ma'adinan da ake fitarwa daga Congo zuwa China ya ƙaru matuƙa, yayin da alkaluma ke nuna cewa tsakanin kashi 80 zuwa 95 cikin 100 na cobalt da ake haƙowa a Congo na ƙarewa ne a China.
Lighthouse Reports da Financial Times sun bayyana cewa har yanzu akwai ƙarancin bayyana gaskiya game da yadda ake haƙowa da kuma fitar da waɗannan ma'adanai daga lardin Katanga. Haka kuma, mujallar Nature Communications ta taba bayyana irin wannan damuwa a wani rahoto, inda ta yi nuni da cewa adadin uranium da aka fitar ba bisa ƙa'ida ba na iya kaiwa kusan tan dubu biyar.
Rahoton ya kuma ambaci wasu kamfanonin hakar ma'adinai da ke aiki a yankin, inda ya ce akwai tambayoyi da ake yi kan yadda suke gudanar da ayyukansu. Sai dai rahoton bai ce an tabbatar da aikata wani laifi daga waɗannan kamfanoni ba.
Idan har waɗannan zarge-zargen suka tabbata, lamarin na iya ƙara jawo hankalin ƙasashen duniya kan yadda ake sa ido da kuma sarrafa fitar da muhimman ma'adanai daga Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo.